Skip to main content

Wajibi ne muyi bincike kan mutuwar Mohammad Mursi - Majalisar dinkin duniya



Shugaban majalisar dinkin duniya, Antonio Guterres ya bada kariya ga kiran da majalisar tayi na gudanar da bincike mai zaman kanta kan mutuwar tsohon shugaban kasar Misra, Mohammed Mursi.


Mataimakin mai magana da yawun shugaban MDD, Haq Farhan, ya bayyanawa kamfanin dillancin Najeriya NAN a birnin New York cewa Antonio Guterres na tare da duk abinda majalisar dinkin duniya ta fadi.



Farhan wanda ya bada amsa kan tambayar cewa shin me majalisar dinkin duniya za ta ce game da martanin kasar Misra cewa ana kokarin siyasantar da mutuwar Mursi.




Muhammad Mursi, shine zababben shugaban kasar Misra na farko a tarihin kasar, ya rasu ranar Litinin a kotu bayan shekara 6 da yi masa juyin mulki da jefashi gidan yari.

A ranar Talata, kwamishanan majalisar dinkin duniya kan kare hakkin dan Adam, ya yi kira ga bincike mai zurfi kan mutuwar Mursi.

A jawabinsa, mai magan da yawunsa, Rupert Colville, ya ce binciken ya game dukkan abubuwan da suka faru da Mursi cikin shekaru shida da aka tsareshi.


Yace: "Ya kamata a gudanar da bincike mai zaman kanta kuma wacce ba tada alaka da kasar da ta tsareshi. Wajibi ne a gudanar da bincike kan abubuwan da suka faru da suka sabbaba mutuwarsa."



Ma'aikatar harkokin wajen Misra ta mayar da martani kan wannan jawabin cewa majalisar dinkin duniya na kokarin sanya baki cikin harkokin kasar da kuma batwa bangaren shari'arta suna.

Mun samu wannan labarin daga kamfanin Liget.com



ko shakka babu wannan babban labari ne Mai cike da faranta rai, muna fatan zai tabbata kuma a bi masa kadin sa.

Muna bada hakuri kasancewar mun yi amfani da hoton shugaba kasar Turkiyya ne ,ba na Majalisar dinkin duniya ba

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...