Skip to main content

Wajibi ne muyi bincike kan mutuwar Mohammad Mursi - Majalisar dinkin duniya



Shugaban majalisar dinkin duniya, Antonio Guterres ya bada kariya ga kiran da majalisar tayi na gudanar da bincike mai zaman kanta kan mutuwar tsohon shugaban kasar Misra, Mohammed Mursi.


Mataimakin mai magana da yawun shugaban MDD, Haq Farhan, ya bayyanawa kamfanin dillancin Najeriya NAN a birnin New York cewa Antonio Guterres na tare da duk abinda majalisar dinkin duniya ta fadi.



Farhan wanda ya bada amsa kan tambayar cewa shin me majalisar dinkin duniya za ta ce game da martanin kasar Misra cewa ana kokarin siyasantar da mutuwar Mursi.




Muhammad Mursi, shine zababben shugaban kasar Misra na farko a tarihin kasar, ya rasu ranar Litinin a kotu bayan shekara 6 da yi masa juyin mulki da jefashi gidan yari.

A ranar Talata, kwamishanan majalisar dinkin duniya kan kare hakkin dan Adam, ya yi kira ga bincike mai zurfi kan mutuwar Mursi.

A jawabinsa, mai magan da yawunsa, Rupert Colville, ya ce binciken ya game dukkan abubuwan da suka faru da Mursi cikin shekaru shida da aka tsareshi.


Yace: "Ya kamata a gudanar da bincike mai zaman kanta kuma wacce ba tada alaka da kasar da ta tsareshi. Wajibi ne a gudanar da bincike kan abubuwan da suka faru da suka sabbaba mutuwarsa."



Ma'aikatar harkokin wajen Misra ta mayar da martani kan wannan jawabin cewa majalisar dinkin duniya na kokarin sanya baki cikin harkokin kasar da kuma batwa bangaren shari'arta suna.

Mun samu wannan labarin daga kamfanin Liget.com



ko shakka babu wannan babban labari ne Mai cike da faranta rai, muna fatan zai tabbata kuma a bi masa kadin sa.

Muna bada hakuri kasancewar mun yi amfani da hoton shugaba kasar Turkiyya ne ,ba na Majalisar dinkin duniya ba

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...