Skip to main content

Manufar Almajiri a Kasar Hausa




Abin da ake nufi da ALMAJIRI a kalmar Hausa, sunan ya samo asali ne a kasar Hausa tin lokacin da addinin musulunci ya fara samun karbuwa a kasar Hausa, har iyaye suka fara amincewa da bada 'ya'yansu karantarwa a makarantun Tsangayoyin Malaman da suka shigo da ilimin addinin Muslinci a kasar Hausa.
Wanda sukayi imani a wancan lokacin, suka watsar da Bautar Aljani Giji a kasar Hausa, sai suke daukar kyautar Tufafi da Abinci Suna baiwa Almajirai saboda neman tsira da amincin Allah.

Kafin zuwan karantarwar addinin musulunci karkashin tsarin (tsangaya) a kasar Hausa, Ana Bautar Aljannu ne, wadanda ake kira da suna(Giji) a kalmar Hausa, kusan kowane gida akwai (Giji), kuma kowace zuri'ah suna da (Giji), duk wata Masarautar da suka kafu a wancen lokacin suna da Babban (Giji) wanda duk Shekara al'ummar Garin suke Bauta masa duk Gari, idan ana neman Biyan Bukata ana Rokon (Giji) domin a samu biyan Bukata a lokacin jahiliyya.


Daga cikin masu wayo a kasar Hausa tuni sun fahimci (Al'jani-giji) baya iya biya musu bukatunsu, sai suka fara imani da (Ubangiji) bi ma'ana Allah Madaukakin Sarki, wasu kuma sun bijire, suka fifita al'adar kasar Hausa na bautar (Al'jani-giji)akan cewa su bazasu iya barin addinin kakaninsu ba.
Lokacin da Addinin (Ubangiji) ya fara karfi a kasar Hausa,  masu bautar (Ubangiji) sun samu mabiya harma sun fara kafa sansani a wasu yankunan kasar Hausa, sai suka daina jihadin fadakarwa aka chanza salon jihadin zuwa yaki da masu bautar (Al'jani-Giji) . Da irin wannan gwagwarmayar mallaman tsangaya suka ruwaito Addinin Allah a kasar Hausa, amma maimakon gwamnati da dubi tsaftacce tsarin sai take kokarin dakatar da tsarin baki daya a kasar Hausa.


Idon aka hana Bara ina makomar marasa galihu? Sanin dukkanin wanda yake a lardin Arewa ne, Al'adar bara ta samo asali ne tun kafin zuwan turawan mulkin mallaka a kasar hausa. Sannan tun a lokaci ana kallon bara a matsayin wata hanya wanda mutum yake bi domin samun abinda zai ci da abinda zai sha, domin tsayuwa haikan wajen neman ilimin addinin musulunci, da samuwar tarbiyya.

Wannan ne yasa ake safarar yara kanana gari-wa-gari kasa-wa-kasa, zuwa wajen asalin malaman zaure domin samun ilimi mai mai nagarta. Kasancewar bara ya kasu kashi biyu, akwai bara na yara masu karatun allo sannan akwai bara na manyan masu neman tara dukiya. Tabbas mafi yawa daga cikin mutanen da yau suke fada aji a fannin falsafar addinin musulunci, sun samu cikakken ilimin addini, wanda shine ya musu tsani kuma ya masu gata har zuwa wannan lokaci, kuma har gobe ana alfahari da su.

Tabbas duk wanda anka ce ya rufe shagonsa wanda yake neman na rufa, to tabbas ya na bukatar a bude masa babban shagon da zai samu na tuwo, wannan haka yake ko shakka babu.

Tun kafin zuwa wajen magance matsalar barace-barace a cikin al'umma, wanda yafi kamari a yankin Arewa, akwai babbar matsalar da ya kamata Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya fara fuskanta domin magance ta, shine ilimin neman abun duniya wato; Ilimin Boko, wanda tun lokacin da anka baiwa Najeriya 'yancin kanta, har yanzu abun yaki daidaita.

Idon mukayi la'akari da irin makarantun Boko ko wadanda suke a cikin birane suna fuskantar babban kalubale, balle wadanda suke a cikin karkara. kama tun daga, littatafan Karatu, dakunan gwaje-gwaje, hadi da rashin isasun Uniform na dalibai da harkar ciyarwa, da daidaita albashin malamai, hadi da tantance malamai masu koyarwa a makarantu daban-daban na kowane bangare, idan ilimin boko ya daidaita sannan a dubi yunkurin kawar da barece-barace a cikin al'umma.



Ilimin addini cilas ne ga kowane musulmi, domin yasan yadda zai bautawa Mahaliccinsa, don ya samu tsira a gobe Kiyama, sannan ko ba kada ko sisin kwabo, dole ne Uba ya kawo dansa a makaranta domin neman ilimin addini.

Idan mukayi dogon nazari akan mafi yawa daga almajirai, wadanda sunka sha wahalar makaranta kuma sun ka sha gwaggwarmayar neman ilimi, mafi yawansu yanzu sun koma manyan mutune, sun kama wata sana'ar ta daban suna ci da kansu da iyalansu da 'yan uwansu da abokan arziki. Kasancewar samun ilimin nan da sun kayi tun da farko.

Babban nauyin da rataya ga wuyan gwamnati da shuwagabannin Arewa, idan har zasu yi yunkurin kawar da bara na almajirai to lallai ko sai sun samar masu da hanyoyin dogaro da kai wanda zasu tsayu da kafafunsu wajen neman halalinsu, wadanda sunka hada da; koya musu sana'o'in hannu, kamar Yankan Kunba, shumeka, sayar da tazbi, hadi da sarrafa ta, sayar da turaruka, da sauransu, wanda ta hakan zasu jefi tsuntsu biyu da dutsi daya. Inko ba haka ba, to lallai akwai wata a kasa.

Muna fatan gwamnatin tarayyar Najeriya karkashin jagoranci shugaba Muhammadu Buhari, da gwamnatocin Arewa za suyi karatun ta natsu, suyi dogon nazari da hangen nesa, wajen aiki da hikima da dabaru irin na mulki wajen magance abinda ake gani matsala.


Babu wata al'umma da bata son ci gaba, saboda haka muna addu'a da fatan alheri ga kasarmu Najeriya da lardin Arewa. Muna addu'ar Allah yayiwa malummanmu albarka da sunka rikawa iyayenmu ba mu cikakkiyar tarbiyya. Allah ya saka musu da mafificin alheri.

Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau. 08133376020

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...