Skip to main content

MU KAWAR DA BARA, DOMIN FARFAƊO DA MARTABARMU A YANKIN AREWA!



Assalamu alaikum,

Sannun mu da warhaka Da fatan alheri ga kowa, ko shakka babu illar barace-barace a cikin al'umma illa ce mai matuƙar hatsarin gaske wanda ya kamata mu hada hannu ƙarfi da ƙarfe domin yaƙarta a cikin al'ummarmu domin samarwa da 'yan bayanmu kyakkyawar makoma.

Addinin musulunci ya koyar da mu yadda zamu kasance mutane nagari a cikin jama'a a inda duk inda muka shiga za'ayi alfahari da mu a ko ina a faɗin duniyar nan, haka ya koyar damu yadda zamuyi mu'amala da har mutanen da ba addininmu ɗaya da su ba. Ya ku 'yan uwa musulmi! Ko shakka babu musulunci bai yadda da bara ba, sai dai akan lalura, Misali wanda yana cikin hali na tafiya sai guzurinsa ya ƙare, wannan musulunci ya yarje masa yayi bara domin ya samu iya adadin abinda zai isa ya kaishi inda yake son yaje.

Sannan wanda yake cikin wani hali na ƙa-ƙa-ni-ka yi, shima wannan an yarje masa yayi bara domin samun ɗan abinda zai tashi da kansa ma'ana ya samu ɗan abun yin sana'a wanda da zarar ya samu to babu shakka bakin nan baran ya haramta gare shi.

ALLAH Maɗaukakin Sarki Yace; "Mun Karrama 'yan Adam" To ashe ko ya za'ayi mu maida kanmu ƙasƙantattu?

A bisa illar da ke akwai a cikin bara, Manzon Allah (S.A.W) ya bamu labari, duk wanda kayin bara kuma har ya Mutu bai tuba ba, a ranar al'ƙiyama zai tashi bashi da naman fuska. mana'a fuskarsa zai tashi da ita ta koma ƙwaranƙwal. Haƙiƙa wannan zai nuna mana illar yin bara domin mu guje Ta mu zauna lafiya da aminci.

Dukan ɗan Adam Akwai baiwar da ALLAH Maɗaukakin Sarki ya yi masa, kuma ya arzutashi da ita cikin iyawarsa da hikimarsa.

Illolin da ke akwai a cikin bara suna da matuƙar yawan gaske wasu daga ciki;-

Yin Bara yana zubarwa da ɗan Adam da mutunci ga idanun al'umma, kasancewar idon mukayi dubo da irin kallon da ake masa, mai naƙasassar Zuciya.

Yin Bara har kullum yana kara sanyawa ɗan Adam Sanyin zuciya wajen rashin kwarin gwiwar tashi ya nemi na kansa, domin cirewa kansa takaici.

Al'ummomi daban-daban a sassa daban-daban na Duniya babu wata al'ummar da babu naƙasassu a cikinta, sannan babu wata ƙasa a duniya da ba ta da marasa ƙarfi, duk da haka basu aminta da yin bara ba, sun dogara ga ALLAH kuma shi yake ciyar da su.

Idon muka dawo a nan cikin gida Najeriya, sai muyi duba a kan wasu daga cikin yankunan Kudancin ƙasar nan, musamman waɗanda ba musulmai ba, za mu ga cewa akwai naƙasassu sosai a cikinsu, amma basu yarda da yin bara ba, amma sun aminta da sana'a komai ƙanƙantarta!

Babbar musifa ce irin yadda a kullum zaka ga 'yan uwanmu a saman tinuna suna tangararo da sunan bara. babban abun damuwa ne irin yadda sunka zubar da martabarmu ga idanun wasu da sunan bara. Babban koma baya ne mu rungumi sana'ar bara, mu zubar da Baiwar da ALLAH yayi mana. Babbar matsala ce mu kasa godiya ga duk halin da munka tsintsi kanmu. Babbar barazana ce a Arewa yin bara.

Muna fatan Gwamnatin tarayyar Najeriya Ƙarƙashin jagoranci mai daraja ta farko a cikin ƙasar nan, kuma mai faɗa aji wato Shugaba Muhammadu Buhari, haɗi da gwamnonin Arewa, da hukumomin Gwamnati da wasu kungiyoyi masu zaman kansu, su zaburo wajen kauda bara a cikin ƙasar nan, domin samarwa da 'yan baya kyakkyawar rayuwa.

Naƙasa ba kasawa ba! Bara ƙasƙanci ne! Mu kawar da bara domin mu samu salama!

ALLAH bai yimu Ƙasƙantattu ba, Balle mu ƙasƙance!!!

Daga Nura Mai Apple Gusau Ɗan Ƙungiyar Mukawar da Bara ta Kasa Reshen Jihar Zamfara +2348133376020



Copyright@maiapplegusau

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020