Skip to main content

BABBAN TARON KUNGIYAR MURYAR TALAKA TA KASA RESHEN JIHAR ZAMFARA KARO NA UKKU YA 'KAYATAR!



Daga; Nura Muhammad Mai Apple, Gusau 

Kasancewar kungiyar muryar talaka ta Kasa reshen jihar Zamfara kusan itace uwa mabada mama ga takwarorinta na wasu jihohin kasar nan, jiya Lahadi 15/04/2018 Tayi babban taronta Wanda ta Saba Duk shekara Wanda Wannan Karon shine karo  na ukku, a cikin jerin kwanon shiraruwanta Wanda ta Saba Yi, Hakika Wannan Karon kusan zamu iya cewa ya samu Gagarumin nasara.

Irin yadda mun kaga shirin ya samu tsari mai kyau, ta hanyar yadda Anka rarraba membobin kungiyar kowane da nashi aiki, mutane da dama sun sauki darasi a cikin bayanan manyan Malamai, kamarsu Dr, Murtala Kaura, da Prof, Jibiya, ko shakka babu irin yadda sunka gabatar da bayanai wajan Abin sai dai Sam Barka.


Hakika 'YA'yan kungiyar muryar talaka reshen jihar Zamfara sun Nuna dattako matuka ainun, irin yadda sunka bada hadin Kai, ankayi Wannan babban Taron lafiya kuma munka kammala lafiya, Duk da wasu daga ciki, sunsu su bata tsarin ta hanyar yin kutse GA ayukan da ba'a sasuba. Amma Duk da haka muna godiya GA Allah da yanuna mana  An kammala ba tare da wata Matsala ba. 


Duk da irin aikin da anka bamu munso mu fuskanci turjiya ga jami'an tsaro, lokacin da munka so dauko wani hoto mai matukar muhimmanci amma kuma sunka hanamu, Kasancewar cincirindon jerin kwanon 'yan jaridu da 'yan Social media,

Mutane da dama sun amfana da Wannan Gagarumin shirin Musamman matasa wadanda sunka samu tallafin kayan sana'o'in hannu, da fatan Allah yasa zasuyi amfani da abinda sunka samu wajan ci gaban Kansu har su tallafawa wadan su, suma suci gajiyar abin.

Muna Addu'ar Allah ya taimaki kungiyar muryar talaka ta Kasa reshen jihar Zamfara da 'YA'yan kungiyar kwata, 


Daga; Nura Muhammad Mai Apple Gusau 



Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...