Skip to main content

BABBAN TARON KUNGIYAR MURYAR TALAKA TA KASA RESHEN JIHAR ZAMFARA KARO NA UKKU YA 'KAYATAR!



Daga; Nura Muhammad Mai Apple, Gusau 

Kasancewar kungiyar muryar talaka ta Kasa reshen jihar Zamfara kusan itace uwa mabada mama ga takwarorinta na wasu jihohin kasar nan, jiya Lahadi 15/04/2018 Tayi babban taronta Wanda ta Saba Duk shekara Wanda Wannan Karon shine karo  na ukku, a cikin jerin kwanon shiraruwanta Wanda ta Saba Yi, Hakika Wannan Karon kusan zamu iya cewa ya samu Gagarumin nasara.

Irin yadda mun kaga shirin ya samu tsari mai kyau, ta hanyar yadda Anka rarraba membobin kungiyar kowane da nashi aiki, mutane da dama sun sauki darasi a cikin bayanan manyan Malamai, kamarsu Dr, Murtala Kaura, da Prof, Jibiya, ko shakka babu irin yadda sunka gabatar da bayanai wajan Abin sai dai Sam Barka.


Hakika 'YA'yan kungiyar muryar talaka reshen jihar Zamfara sun Nuna dattako matuka ainun, irin yadda sunka bada hadin Kai, ankayi Wannan babban Taron lafiya kuma munka kammala lafiya, Duk da wasu daga ciki, sunsu su bata tsarin ta hanyar yin kutse GA ayukan da ba'a sasuba. Amma Duk da haka muna godiya GA Allah da yanuna mana  An kammala ba tare da wata Matsala ba. 


Duk da irin aikin da anka bamu munso mu fuskanci turjiya ga jami'an tsaro, lokacin da munka so dauko wani hoto mai matukar muhimmanci amma kuma sunka hanamu, Kasancewar cincirindon jerin kwanon 'yan jaridu da 'yan Social media,

Mutane da dama sun amfana da Wannan Gagarumin shirin Musamman matasa wadanda sunka samu tallafin kayan sana'o'in hannu, da fatan Allah yasa zasuyi amfani da abinda sunka samu wajan ci gaban Kansu har su tallafawa wadan su, suma suci gajiyar abin.

Muna Addu'ar Allah ya taimaki kungiyar muryar talaka ta Kasa reshen jihar Zamfara da 'YA'yan kungiyar kwata, 


Daga; Nura Muhammad Mai Apple Gusau 



Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.