Skip to main content

BABBAN TARON KUNGIYAR MURYAR TALAKA TA KASA RESHEN JIHAR ZAMFARA KARO NA UKKU YA 'KAYATAR!



Daga; Nura Muhammad Mai Apple, Gusau 

Kasancewar kungiyar muryar talaka ta Kasa reshen jihar Zamfara kusan itace uwa mabada mama ga takwarorinta na wasu jihohin kasar nan, jiya Lahadi 15/04/2018 Tayi babban taronta Wanda ta Saba Duk shekara Wanda Wannan Karon shine karo  na ukku, a cikin jerin kwanon shiraruwanta Wanda ta Saba Yi, Hakika Wannan Karon kusan zamu iya cewa ya samu Gagarumin nasara.

Irin yadda mun kaga shirin ya samu tsari mai kyau, ta hanyar yadda Anka rarraba membobin kungiyar kowane da nashi aiki, mutane da dama sun sauki darasi a cikin bayanan manyan Malamai, kamarsu Dr, Murtala Kaura, da Prof, Jibiya, ko shakka babu irin yadda sunka gabatar da bayanai wajan Abin sai dai Sam Barka.


Hakika 'YA'yan kungiyar muryar talaka reshen jihar Zamfara sun Nuna dattako matuka ainun, irin yadda sunka bada hadin Kai, ankayi Wannan babban Taron lafiya kuma munka kammala lafiya, Duk da wasu daga ciki, sunsu su bata tsarin ta hanyar yin kutse GA ayukan da ba'a sasuba. Amma Duk da haka muna godiya GA Allah da yanuna mana  An kammala ba tare da wata Matsala ba. 


Duk da irin aikin da anka bamu munso mu fuskanci turjiya ga jami'an tsaro, lokacin da munka so dauko wani hoto mai matukar muhimmanci amma kuma sunka hanamu, Kasancewar cincirindon jerin kwanon 'yan jaridu da 'yan Social media,

Mutane da dama sun amfana da Wannan Gagarumin shirin Musamman matasa wadanda sunka samu tallafin kayan sana'o'in hannu, da fatan Allah yasa zasuyi amfani da abinda sunka samu wajan ci gaban Kansu har su tallafawa wadan su, suma suci gajiyar abin.

Muna Addu'ar Allah ya taimaki kungiyar muryar talaka ta Kasa reshen jihar Zamfara da 'YA'yan kungiyar kwata, 


Daga; Nura Muhammad Mai Apple Gusau 



Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020