Skip to main content

Janar Ibrahim Babangida Ya Yi Wa Jam’iyyar PDP Fatan Alheri



Tsohon shugaban Najeriya na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida IBB, ya yi wa jam’iyyar adawa ta PDP fatan alheri yayin da take kokarin shirya babban taronta na kasa inda za ta zabi sabbin shugabanninta a karshen wannan mako.

A cewar tsohon shugaba Ibrahim Badamasi Babangida hankalinsa na wurin taron kasa da jam’yyar PDP ke shirin gudanarwa ranar wannan Asabar mai zuwa. Fatansa shi ne a kammala taron lafiya.

Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya kira taron manema labarai ne a Minna domin yiwa dubban ‘yan kasuwar tsohuwar Panteka dake Kaduna da suka tafka asarar miliyoyin Nera sakamakon gobarar da ta lakume kasuwar, lokacin ne ya yi furucinsa akan PDP.

Tsohon shugaban yana fatan ‘yan jam’iyyar zasu kai zuciya nesa a taronsu tare da rungumar kaddarar shan kaye. Yana cewa “Na yi masu kyakyawan fata. Ina son duk yadda za’a yi… tunda siyasa ake, wasu su ci, wasu ba zasu ci ba. Wanda ya ci ya dauka haka Allah ya yi. Sun ci kuma aiki ne na jama’a”.

A cewar tsohon shugaban muddin wadanda aka zaba sun yiwa jama’a aiki bukata ta biya tare da kara fatan Allah ya sa su yi taro lafiya su kuma tashi lafiya.

Janar Babangida ya na da ra’ayin cewa yin adalci ga sabbin shugabannin da za’a zaba su karbi shugabancin jam’iyyar ya na da matukar tasiri wajen tunkarar babban zabe mai zuwa. Ya ce a matsayinsu na shugabannin kamata ya yi jam’iyyar ta nemi shugabanni masu adalci, masu gaskiya, masu fasaha da suka amince da siyasa. Sun san kanta kuma zasu taimakawa magoya bayansu.

Dangane da komawar Alhaji Atiku Abubakar jam’iyyar PDP, Janar Babangida ya ce tsarin mulkin kasa ya bashi hurumin yin hakan tare da iya shiga kowace jam’iyya.

Kawo yanzu mutane takwas ne ke neman kujerar shugabancin jam’iyyar ta PDP.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.