Skip to main content

Janar Ibrahim Babangida Ya Yi Wa Jam’iyyar PDP Fatan Alheri



Tsohon shugaban Najeriya na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida IBB, ya yi wa jam’iyyar adawa ta PDP fatan alheri yayin da take kokarin shirya babban taronta na kasa inda za ta zabi sabbin shugabanninta a karshen wannan mako.

A cewar tsohon shugaba Ibrahim Badamasi Babangida hankalinsa na wurin taron kasa da jam’yyar PDP ke shirin gudanarwa ranar wannan Asabar mai zuwa. Fatansa shi ne a kammala taron lafiya.

Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya kira taron manema labarai ne a Minna domin yiwa dubban ‘yan kasuwar tsohuwar Panteka dake Kaduna da suka tafka asarar miliyoyin Nera sakamakon gobarar da ta lakume kasuwar, lokacin ne ya yi furucinsa akan PDP.

Tsohon shugaban yana fatan ‘yan jam’iyyar zasu kai zuciya nesa a taronsu tare da rungumar kaddarar shan kaye. Yana cewa “Na yi masu kyakyawan fata. Ina son duk yadda za’a yi… tunda siyasa ake, wasu su ci, wasu ba zasu ci ba. Wanda ya ci ya dauka haka Allah ya yi. Sun ci kuma aiki ne na jama’a”.

A cewar tsohon shugaban muddin wadanda aka zaba sun yiwa jama’a aiki bukata ta biya tare da kara fatan Allah ya sa su yi taro lafiya su kuma tashi lafiya.

Janar Babangida ya na da ra’ayin cewa yin adalci ga sabbin shugabannin da za’a zaba su karbi shugabancin jam’iyyar ya na da matukar tasiri wajen tunkarar babban zabe mai zuwa. Ya ce a matsayinsu na shugabannin kamata ya yi jam’iyyar ta nemi shugabanni masu adalci, masu gaskiya, masu fasaha da suka amince da siyasa. Sun san kanta kuma zasu taimakawa magoya bayansu.

Dangane da komawar Alhaji Atiku Abubakar jam’iyyar PDP, Janar Babangida ya ce tsarin mulkin kasa ya bashi hurumin yin hakan tare da iya shiga kowace jam’iyya.

Kawo yanzu mutane takwas ne ke neman kujerar shugabancin jam’iyyar ta PDP.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...