Skip to main content

Janar Ibrahim Babangida Ya Yi Wa Jam’iyyar PDP Fatan Alheri



Tsohon shugaban Najeriya na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida IBB, ya yi wa jam’iyyar adawa ta PDP fatan alheri yayin da take kokarin shirya babban taronta na kasa inda za ta zabi sabbin shugabanninta a karshen wannan mako.

A cewar tsohon shugaba Ibrahim Badamasi Babangida hankalinsa na wurin taron kasa da jam’yyar PDP ke shirin gudanarwa ranar wannan Asabar mai zuwa. Fatansa shi ne a kammala taron lafiya.

Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya kira taron manema labarai ne a Minna domin yiwa dubban ‘yan kasuwar tsohuwar Panteka dake Kaduna da suka tafka asarar miliyoyin Nera sakamakon gobarar da ta lakume kasuwar, lokacin ne ya yi furucinsa akan PDP.

Tsohon shugaban yana fatan ‘yan jam’iyyar zasu kai zuciya nesa a taronsu tare da rungumar kaddarar shan kaye. Yana cewa “Na yi masu kyakyawan fata. Ina son duk yadda za’a yi… tunda siyasa ake, wasu su ci, wasu ba zasu ci ba. Wanda ya ci ya dauka haka Allah ya yi. Sun ci kuma aiki ne na jama’a”.

A cewar tsohon shugaban muddin wadanda aka zaba sun yiwa jama’a aiki bukata ta biya tare da kara fatan Allah ya sa su yi taro lafiya su kuma tashi lafiya.

Janar Babangida ya na da ra’ayin cewa yin adalci ga sabbin shugabannin da za’a zaba su karbi shugabancin jam’iyyar ya na da matukar tasiri wajen tunkarar babban zabe mai zuwa. Ya ce a matsayinsu na shugabannin kamata ya yi jam’iyyar ta nemi shugabanni masu adalci, masu gaskiya, masu fasaha da suka amince da siyasa. Sun san kanta kuma zasu taimakawa magoya bayansu.

Dangane da komawar Alhaji Atiku Abubakar jam’iyyar PDP, Janar Babangida ya ce tsarin mulkin kasa ya bashi hurumin yin hakan tare da iya shiga kowace jam’iyya.

Kawo yanzu mutane takwas ne ke neman kujerar shugabancin jam’iyyar ta PDP.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020