Skip to main content

Gwamnatin Tarayya Ta Bawa David Mark Wa’Adin Kwanaki 21 Ya Tattara Nasa-Ya-Nasa Ya Fice Daga Gidan Shugaban Majalisar Dattijai



Gwamnatin tarayya ta zargi tsohon shugaban majalisar dattijai, David Mark, da mallakar gidan shugaban majalisar ta haramtacciyar hanya.

Kwamitin bincike da kwato kadarorin gwamnatin tarayya da ofishin shugaban kasa ya kafa a watan Satumba karkashin jagorancin Cif Okoi Obono-Obla ya gano hakan kuma ya dibawa Mark wa’adin kwanaki 21 ya tattara nasa ya nasa ya bar gidan.

Tsohon Shugaban Majalisar Dattijai David Mark
A cikin takardar wa’adin kwanakin barin gidan da kwamitin ya aikewa Mark, an bukaci da ya gabatar da wata hujja, idan yana da ita, da zata hana gwamnati fitar da shi daga gidan.

Saidai David Mark ya garzaya babban kotun tarayya dake Abuja domin dakatar da gwamnatin daga fitar da shi daga gidan da kuma kwace mallakin gidan daga hannun sa.

DUBA WANNAN: Kotu ta yankewa wani maigadi hukuncin zaman gidan yari na wata shida bisa laifin yin barci yayin aiki
Har yanzu kotun bata saurari karar da Mark ya shigar gaban na ta ba.

Gidan shugaban majalisar dattijai dake kan titin Chuba Okadigbo a yankin rukunin gidajen ‘yan majalisu dake Apo a Abuja, yana da girman hekta 1.6 dauke da gidaje guda takwas, a warware da juna, a ciki.

David Mark, Sanatan Najeriya daga jihar Benuwe, ya kasance shugaban majalisar dattijai kafin jam’iyyar sa ta PDP ta fadi zabe a Najeriya ta kuma rasa rinjaye a majalisa.

Kwamitin ya zargi cewar Mark ya mallakawa kan sa gidan ne yayin da yake shugabancin majalisar a kan farashi mai rahusa. An yi kiyasin cewar gidan shugaban majalisar yana da darajar data ketare Naira miliyan 748 a farashi mai rangwame.

Gwamnatin tarayya ta bawa David Mark wa’adin kwanaki 21 ya tattara nasa-ya-nasa ya fice daga gidan shugaban majalisar dattijai

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...