Skip to main content

Ban Taba Ganawa Da Buhari Ba, Jibrin Ya Mayar Da Martani Ga Dogara



Tsohon ciyaman na kwamitin ‘yan majalisar wakilai akan kasafin kudin kasa, Abdulmumin Jibrin, ya bayyana cewa shugaba Buhari bai taba tuntubar sa ba akan tuhumar da yake yiwa shugaban majalisar wakilai, Honorabul Yakubu Dogara, da cewar ya kulla wata makekashiya a cikin kasafin kudi na shekarar 2016.

NAIJ.com ta fahimci cewa, Jibrin ya tuhumi shugaban na majalisar wakilai da kulla wata makekashiya akan kasafin kudi na shekarar 2016 da suka tasar ma Naira miliyan 284.

A cikin wani rubutaccen littafi na tarihin rayuwar Dogara wanda Dele Momodu ya wallafa, shugaban na majalisar wakilai ya bayyana cewa, Buhari ya gargadi Honorabul Jibrin akan kar ya sake tunkarar sa da wannan lamari.

A kalaman Dogara, “Kasancewar shugaba Buhari mai tsari da hangen nesa, ya bukaci masaniya ta inda sauran shugabannin majalisar wakilai suka shiga a yayin da shugabanni hudu suka kebance wajen yin surkulle akan kasafin kudin.”

“Babu ko mutum guda dake yi mana wannan fassara da zasu iya bayar da amsar wannan tambaya. Tun da dai kowa yana da idanu na basira, matukar babu amsa ta wannan tambayar to baya bukatar a sake tunkarar sa da wannan batu.”

KARANTA KUMA: Siyasar 2019: Atiku ya fara tuntubar gwamnoni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP

A yayin mayar da martani akan batutuwan Dogara da Jibrin yayi a ranar Larabar da ta gabata ya bayyana cewa, akwai rubutattun wasiku har guda uku da ya aikawa shugaban kasa, sai dai babu ko guda da ya samu amsar ta.

Ya kara da cewa, ya fahimci cewa akwai wani shinge da Dogara ya gindaya masa a tsakanin sa da shugaba Buhari, saboda haka ya ci gaba da fafutikar bayyanar da gaskiya a karan kan sa, ya kuma dakatar da kokarin sa na neman ganawa da shugaba kasa.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...