Skip to main content

Ban Taba Ganawa Da Buhari Ba, Jibrin Ya Mayar Da Martani Ga Dogara



Tsohon ciyaman na kwamitin ‘yan majalisar wakilai akan kasafin kudin kasa, Abdulmumin Jibrin, ya bayyana cewa shugaba Buhari bai taba tuntubar sa ba akan tuhumar da yake yiwa shugaban majalisar wakilai, Honorabul Yakubu Dogara, da cewar ya kulla wata makekashiya a cikin kasafin kudi na shekarar 2016.

NAIJ.com ta fahimci cewa, Jibrin ya tuhumi shugaban na majalisar wakilai da kulla wata makekashiya akan kasafin kudi na shekarar 2016 da suka tasar ma Naira miliyan 284.

A cikin wani rubutaccen littafi na tarihin rayuwar Dogara wanda Dele Momodu ya wallafa, shugaban na majalisar wakilai ya bayyana cewa, Buhari ya gargadi Honorabul Jibrin akan kar ya sake tunkarar sa da wannan lamari.

A kalaman Dogara, “Kasancewar shugaba Buhari mai tsari da hangen nesa, ya bukaci masaniya ta inda sauran shugabannin majalisar wakilai suka shiga a yayin da shugabanni hudu suka kebance wajen yin surkulle akan kasafin kudin.”

“Babu ko mutum guda dake yi mana wannan fassara da zasu iya bayar da amsar wannan tambaya. Tun da dai kowa yana da idanu na basira, matukar babu amsa ta wannan tambayar to baya bukatar a sake tunkarar sa da wannan batu.”

KARANTA KUMA: Siyasar 2019: Atiku ya fara tuntubar gwamnoni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP

A yayin mayar da martani akan batutuwan Dogara da Jibrin yayi a ranar Larabar da ta gabata ya bayyana cewa, akwai rubutattun wasiku har guda uku da ya aikawa shugaban kasa, sai dai babu ko guda da ya samu amsar ta.

Ya kara da cewa, ya fahimci cewa akwai wani shinge da Dogara ya gindaya masa a tsakanin sa da shugaba Buhari, saboda haka ya ci gaba da fafutikar bayyanar da gaskiya a karan kan sa, ya kuma dakatar da kokarin sa na neman ganawa da shugaba kasa.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

Ta kashe Mijin ta na aure

Ta kashe Mijin ta na aure Jami'an 'Yan Sanda sun damke wata mata mai shekara 42 ta kashe Mijin ta na aure a wata Unguwa a Garin Legas. Ana zargin Folashade Idoko da kashe Mijin ta a cikin gidan su. Jaridar Daily Post tace wannan mummunan abu ya faru ne a cikin Oto-Awori na Garin Legas. Marigayin dai Injiniya ne kuma tuni dai Jamia'an 'Yan Sanda su kayi ram da wannan mata. Mai gidan hayan da Iyalin su ke yace matar wanda malamar asibiti ce ta dade su na samun matsala da Mijin na ta amma yana hakuri. Kuma dai akwai kishin-kishin din cewa kishin jaraba ne ya sa ta kashe Mijin na ta. Matar dai tace tsautsayi aka samu wuka ta fadi a jikin sa ya mutu. Jami’an tsaro sun damke wani saurayi Ifeanyi Chukwu Maxwell Dike dauke da jikin wata yarinya da aka sace a makon jiya.