Skip to main content

Zaben 2019: Gwamnatin Buhari Tana Barazana Ga Hadin Kan Kasa – Inji Atiku



Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari a matsayin babban barazana ga hadin kan kasa, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito. Majiyar mu ta tattara cewa Atiku ya rubuta wasika zuwa ga jam’iyyar APC, inda yake sanar da su shawararsa na ficewa daga jam’iyyar.

Ko da yake ya rubuta wannan wasiƙar ne a ranar 18 ga Oktoba, 2017, amma shugaban jam’iyya mai mulki ta APC a ranar Juma’a ya karyata karbar wannan sanarwa daga tsohon mataimakin shugaban.

A cikin wasikar, Atiku ya ce shawar ficewa daga jam’iyyar bai kasance game da shi ba, amma game da makomar kasar Najeriya.

“Na gagara fahimtar rashin aikin wannan gwamnatin jam’iyya mai mulki, musamman ma game da yadda al’amuran mutanen mu ke ta barbarewa ta hanyar kabilanci da addini wanda ke barazana ga hadin kanmu fiye da kowane lokaci a cikin ‘yan kwanan nan da kuma kalubale da al’ummar kasar ke fuskanta sakamakon durkushewar tattalin arziki”, in ji shi.

A cikin wasikar wanda Usman Muazu ya amince da shi, wanda kuma majiyar NAIJ.com ta samu, Wazirin Adamawa ya ce; “Ina so in sanar da ku game da shawarar yin murabus daga jam’iyyar APC a wannan rukunin wanda kuma za ta fara daga ranar da wannan wasika ta fito”.

“Na yi murabus daga wannan jam’iyyar da muka kafa kuma muka yi tsayin daka tare da ‘yan’uwanmu’ na siyasa a duk faɗin ƙasar, don mu sanya gwamnati. Ina fata cewa a wancan lokacin gwamnatin APC za ta inganta rayuwar jama’armu da ci gaban Najeriya a matsayin al’umma guda ɗaya. Amma wannan buri ta riga ta rushe”.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...