Skip to main content

Zaben 2019: Gwamnatin Buhari Tana Barazana Ga Hadin Kan Kasa – Inji Atiku



Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari a matsayin babban barazana ga hadin kan kasa, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito. Majiyar mu ta tattara cewa Atiku ya rubuta wasika zuwa ga jam’iyyar APC, inda yake sanar da su shawararsa na ficewa daga jam’iyyar.

Ko da yake ya rubuta wannan wasiƙar ne a ranar 18 ga Oktoba, 2017, amma shugaban jam’iyya mai mulki ta APC a ranar Juma’a ya karyata karbar wannan sanarwa daga tsohon mataimakin shugaban.

A cikin wasikar, Atiku ya ce shawar ficewa daga jam’iyyar bai kasance game da shi ba, amma game da makomar kasar Najeriya.

“Na gagara fahimtar rashin aikin wannan gwamnatin jam’iyya mai mulki, musamman ma game da yadda al’amuran mutanen mu ke ta barbarewa ta hanyar kabilanci da addini wanda ke barazana ga hadin kanmu fiye da kowane lokaci a cikin ‘yan kwanan nan da kuma kalubale da al’ummar kasar ke fuskanta sakamakon durkushewar tattalin arziki”, in ji shi.

A cikin wasikar wanda Usman Muazu ya amince da shi, wanda kuma majiyar NAIJ.com ta samu, Wazirin Adamawa ya ce; “Ina so in sanar da ku game da shawarar yin murabus daga jam’iyyar APC a wannan rukunin wanda kuma za ta fara daga ranar da wannan wasika ta fito”.

“Na yi murabus daga wannan jam’iyyar da muka kafa kuma muka yi tsayin daka tare da ‘yan’uwanmu’ na siyasa a duk faɗin ƙasar, don mu sanya gwamnati. Ina fata cewa a wancan lokacin gwamnatin APC za ta inganta rayuwar jama’armu da ci gaban Najeriya a matsayin al’umma guda ɗaya. Amma wannan buri ta riga ta rushe”.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.