Skip to main content

Najeriya Ce Kan Gaba Wajen Samar Da Iri Na Noma A Yankin Afirka Ta Yamma – NASC



Shugaban cibiyar samar da iri na noma ta NASC (National Agricultural Seeds Council), Mista Philip O. Ojo, ya bayyana cewa, kasar Najeriya ce ke samar da kashi 75 na iri na noma da ake amfani da shi a gaba daya yankin Afirka ta Yamma, wanda hakan ya maishe da kasar kan gaba wajen samar da iri na noma a yankin.

Mista Philip ya bayyana hakan ne yayin da ya jagoranci tawagar cibiyar da ta ziyarci gwamnan jihar Jigawa Alhaji Badaru Abubakar, a ranar Litinin din da ta gabata.
Shugaban cibiyar ya bayar da jawabi da cewar, “kasar Najeriya ce ka samar da kaso 75 na irin shuka da ake amfani da shi a yankin Afirka ta Yamma, wanda hakan ya maishe da ita kan gaba wajen fitar da iri zuwa kasashen ketare dake nahiyyar.

Najeriya ce kan gaba wajen samar da iri na noma a yankin Afirka ta Yamma – NASC
“Wannan shine bigire da kasar ta yi fintikau, amma muna bukatar ta kara hobbasa yinkurin ta. Sai dai irin taimako da gudunmawa da wasu jihohin kasar suke bayar wa abin yabawa ne, kuma muna kyautata zaton wannan jihohi za su ci ribar gudunmawar da suke bayar wa.”

Mista Ojo ya kara da cewa, kamfanin iri da aka assasa kafa shi a jihar Jigawa alamu ne samar da cigaba domin inganta harkokin noma da gwamnatin jihar take yi.

A nasa jawabin gwamna Badaru ya bayyana cewa, samuwar iri managarta zai taimakawa jihar sa wajen inganta harkokin noma a dukkan wani sashe na ta, ya kuma hanya mafificiya wajen samun albarkar noma tana farawa ne da managartattun iri na shuka.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

Ta kashe Mijin ta na aure

Ta kashe Mijin ta na aure Jami'an 'Yan Sanda sun damke wata mata mai shekara 42 ta kashe Mijin ta na aure a wata Unguwa a Garin Legas. Ana zargin Folashade Idoko da kashe Mijin ta a cikin gidan su. Jaridar Daily Post tace wannan mummunan abu ya faru ne a cikin Oto-Awori na Garin Legas. Marigayin dai Injiniya ne kuma tuni dai Jamia'an 'Yan Sanda su kayi ram da wannan mata. Mai gidan hayan da Iyalin su ke yace matar wanda malamar asibiti ce ta dade su na samun matsala da Mijin na ta amma yana hakuri. Kuma dai akwai kishin-kishin din cewa kishin jaraba ne ya sa ta kashe Mijin na ta. Matar dai tace tsautsayi aka samu wuka ta fadi a jikin sa ya mutu. Jami’an tsaro sun damke wani saurayi Ifeanyi Chukwu Maxwell Dike dauke da jikin wata yarinya da aka sace a makon jiya.