Skip to main content

Najeriya Ce Kan Gaba Wajen Samar Da Iri Na Noma A Yankin Afirka Ta Yamma – NASC



Shugaban cibiyar samar da iri na noma ta NASC (National Agricultural Seeds Council), Mista Philip O. Ojo, ya bayyana cewa, kasar Najeriya ce ke samar da kashi 75 na iri na noma da ake amfani da shi a gaba daya yankin Afirka ta Yamma, wanda hakan ya maishe da kasar kan gaba wajen samar da iri na noma a yankin.

Mista Philip ya bayyana hakan ne yayin da ya jagoranci tawagar cibiyar da ta ziyarci gwamnan jihar Jigawa Alhaji Badaru Abubakar, a ranar Litinin din da ta gabata.
Shugaban cibiyar ya bayar da jawabi da cewar, “kasar Najeriya ce ka samar da kaso 75 na irin shuka da ake amfani da shi a yankin Afirka ta Yamma, wanda hakan ya maishe da ita kan gaba wajen fitar da iri zuwa kasashen ketare dake nahiyyar.

Najeriya ce kan gaba wajen samar da iri na noma a yankin Afirka ta Yamma – NASC
“Wannan shine bigire da kasar ta yi fintikau, amma muna bukatar ta kara hobbasa yinkurin ta. Sai dai irin taimako da gudunmawa da wasu jihohin kasar suke bayar wa abin yabawa ne, kuma muna kyautata zaton wannan jihohi za su ci ribar gudunmawar da suke bayar wa.”

Mista Ojo ya kara da cewa, kamfanin iri da aka assasa kafa shi a jihar Jigawa alamu ne samar da cigaba domin inganta harkokin noma da gwamnatin jihar take yi.

A nasa jawabin gwamna Badaru ya bayyana cewa, samuwar iri managarta zai taimakawa jihar sa wajen inganta harkokin noma a dukkan wani sashe na ta, ya kuma hanya mafificiya wajen samun albarkar noma tana farawa ne da managartattun iri na shuka.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...