Skip to main content

Najeriya Ce Kan Gaba Wajen Samar Da Iri Na Noma A Yankin Afirka Ta Yamma – NASC



Shugaban cibiyar samar da iri na noma ta NASC (National Agricultural Seeds Council), Mista Philip O. Ojo, ya bayyana cewa, kasar Najeriya ce ke samar da kashi 75 na iri na noma da ake amfani da shi a gaba daya yankin Afirka ta Yamma, wanda hakan ya maishe da kasar kan gaba wajen samar da iri na noma a yankin.

Mista Philip ya bayyana hakan ne yayin da ya jagoranci tawagar cibiyar da ta ziyarci gwamnan jihar Jigawa Alhaji Badaru Abubakar, a ranar Litinin din da ta gabata.
Shugaban cibiyar ya bayar da jawabi da cewar, “kasar Najeriya ce ka samar da kaso 75 na irin shuka da ake amfani da shi a yankin Afirka ta Yamma, wanda hakan ya maishe da ita kan gaba wajen fitar da iri zuwa kasashen ketare dake nahiyyar.

Najeriya ce kan gaba wajen samar da iri na noma a yankin Afirka ta Yamma – NASC
“Wannan shine bigire da kasar ta yi fintikau, amma muna bukatar ta kara hobbasa yinkurin ta. Sai dai irin taimako da gudunmawa da wasu jihohin kasar suke bayar wa abin yabawa ne, kuma muna kyautata zaton wannan jihohi za su ci ribar gudunmawar da suke bayar wa.”

Mista Ojo ya kara da cewa, kamfanin iri da aka assasa kafa shi a jihar Jigawa alamu ne samar da cigaba domin inganta harkokin noma da gwamnatin jihar take yi.

A nasa jawabin gwamna Badaru ya bayyana cewa, samuwar iri managarta zai taimakawa jihar sa wajen inganta harkokin noma a dukkan wani sashe na ta, ya kuma hanya mafificiya wajen samun albarkar noma tana farawa ne da managartattun iri na shuka.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.