Skip to main content
Najeriya C

Gwamnatin Najeriya ta bukaci cibiyoyi masu zaman kansu dasu hada kai da jami’an gwamnati na kiwon lafiya domin yaki da zazzabin cizon sauro.
Likitoci a Najeriya, sunce yanzu an daina amfani da tsofaffin magunguna irin su Chloroquine da Fansidar wajen maganin zazzabin cizon sauro domin sun daina tasiri.

Yanzu dai an kawo sabuwar kwayar maganin yaki da maleriya ta ACT, wadda babban sinadarin cikinta shine Artemisinin, dake taimakawa wajen rabuwa da wannan cuta da sauro ke haddasawa. Jami’in yaki da Malaria na Najeriya, malam Abdu Muhammad, yace yara talatin (30) ke mutuwa a a cikin ko wani sa’a daya a Najeriya sanadiyar zazzabin cizon sauro.

Hukumar yara ta Majalisar Dinkin Duniya, tace duk wuni malaria na kashe yara ‘yan kasa da shekara biyar su dubu biyu da dari uku a Najeriya, abinda yasa Najeriya, ta zama kasa ta biyu a yawan mutuwar yara ‘yan kasa da shekaru biyar a duniya.
Jami’in yaki da zazzabin na hukumar lafiya ta duniya a Najeriya (WHO) Rex yace gara a dage ana yin rigakafin kamuwa da cutar ta hanyar amfani da gidan sauron da aka masa feshin magani domin samun kariya.

Kamfanin har-hada magungunan kashe kwari da ake kira Morten, ya baje magunguna da yake sarrafawa, ganin yadda sauro ya addabi al’ummar Najeriya. Jami’in kamfanin Raul Murgai, yace dole a hana yaduwar Sauron ta hanyar feshin magani.

Jami’an duba-gari na ba da shawarar rigakafin cutar ta hanyar amfani da gidan sauro da kuma tsaftace muhalli. Najeriya, ta samu nasarar rage illar zazzabin cizon sauro daga kashi arba’in da biyu cikin dari zuwa ashirin da bakwai cikin dari cikin shekaru hudu da suka wuce

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...