Skip to main content
Najeriya C

Gwamnatin Najeriya ta bukaci cibiyoyi masu zaman kansu dasu hada kai da jami’an gwamnati na kiwon lafiya domin yaki da zazzabin cizon sauro.
Likitoci a Najeriya, sunce yanzu an daina amfani da tsofaffin magunguna irin su Chloroquine da Fansidar wajen maganin zazzabin cizon sauro domin sun daina tasiri.

Yanzu dai an kawo sabuwar kwayar maganin yaki da maleriya ta ACT, wadda babban sinadarin cikinta shine Artemisinin, dake taimakawa wajen rabuwa da wannan cuta da sauro ke haddasawa. Jami’in yaki da Malaria na Najeriya, malam Abdu Muhammad, yace yara talatin (30) ke mutuwa a a cikin ko wani sa’a daya a Najeriya sanadiyar zazzabin cizon sauro.

Hukumar yara ta Majalisar Dinkin Duniya, tace duk wuni malaria na kashe yara ‘yan kasa da shekara biyar su dubu biyu da dari uku a Najeriya, abinda yasa Najeriya, ta zama kasa ta biyu a yawan mutuwar yara ‘yan kasa da shekaru biyar a duniya.
Jami’in yaki da zazzabin na hukumar lafiya ta duniya a Najeriya (WHO) Rex yace gara a dage ana yin rigakafin kamuwa da cutar ta hanyar amfani da gidan sauron da aka masa feshin magani domin samun kariya.

Kamfanin har-hada magungunan kashe kwari da ake kira Morten, ya baje magunguna da yake sarrafawa, ganin yadda sauro ya addabi al’ummar Najeriya. Jami’in kamfanin Raul Murgai, yace dole a hana yaduwar Sauron ta hanyar feshin magani.

Jami’an duba-gari na ba da shawarar rigakafin cutar ta hanyar amfani da gidan sauro da kuma tsaftace muhalli. Najeriya, ta samu nasarar rage illar zazzabin cizon sauro daga kashi arba’in da biyu cikin dari zuwa ashirin da bakwai cikin dari cikin shekaru hudu da suka wuce

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.