Skip to main content

Kimanin Mutane 40,000 Neke Neman Aikin Malanta A Jihar Kaduna



A jiya Alhamis ne Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya bayyana cewa kimanin mutane 40,000 suka mika takardun su ne neman aikin malanta a makarantun gwamnati da ke Jihar.

Gwamnan ya fadi wannan maganan ne kwanaki kadan bayan ya bayyana cewa gwamnatin sa zata sallami malamai makarantun firmare guda 21,780 wanda suka fadi jarabawar cacanta aiki da gwamnatin Jihar ta gudanar.

Kimanin mutane 40,000 ne ke neman aikin malanta a Jihar Kaduna
Hakan ne yasa gwamnatin Jihar tace zata maye gurbin malaman da zata sallama duk da cewa hakan bai yiwa mutane da yawa dadi ba har ma da kungiyar kwadigo na Jihar wanda ta jagoranci zanga-zangar lumana na nuna kin amincewa da sallamar malaman da gwamnatin Jihar ke niyyar yi.

Wata sanarwa da ta fito daga mai baiwa gwamnan Jihar Kaduna shawara kan kafafen yada labarai, Samuel Aruwan tace gwamnan ya bayyana adaddin masu neman aikin ne yayinda yake ganawa da ‘Yan Majalisar Tarayyah a Abuja a ranar Laraba.

Sanarwan ta cigaba da cewa El-Rufai ya roki ‘Yan Majalisar su taimaka su ceto al’ummar da zasu zo nan gaba ta hanyar basu ingantacen ilimi. Ya kuma kara da cewa duk wanda sukayi nasarar cin jarabawar da gwamnatin zatayi zasu samun horo na musamman kafin a tura su makarantun domin su fara koyarwa.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

Ta kashe Mijin ta na aure

Ta kashe Mijin ta na aure Jami'an 'Yan Sanda sun damke wata mata mai shekara 42 ta kashe Mijin ta na aure a wata Unguwa a Garin Legas. Ana zargin Folashade Idoko da kashe Mijin ta a cikin gidan su. Jaridar Daily Post tace wannan mummunan abu ya faru ne a cikin Oto-Awori na Garin Legas. Marigayin dai Injiniya ne kuma tuni dai Jamia'an 'Yan Sanda su kayi ram da wannan mata. Mai gidan hayan da Iyalin su ke yace matar wanda malamar asibiti ce ta dade su na samun matsala da Mijin na ta amma yana hakuri. Kuma dai akwai kishin-kishin din cewa kishin jaraba ne ya sa ta kashe Mijin na ta. Matar dai tace tsautsayi aka samu wuka ta fadi a jikin sa ya mutu. Jami’an tsaro sun damke wani saurayi Ifeanyi Chukwu Maxwell Dike dauke da jikin wata yarinya da aka sace a makon jiya.