Skip to main content

Gusau: Zamfara Ta Sami Sabuwar Kwamishinan ‘Yan Sanda



Sabon kwamishinan ‘yan sanda na jihar Zamfara, Mista Kenneth Ebrimson ya fara aiki.

Ebrimson, ya kasance daga sashin ayyuka na musamman a hedkwatar hukumar ‘yan sanda kuma ya maye gurbin tsohon kwamishina, Alhaji Shaba Alkali wanda aka sake dawo da shi a hedkwatar da ke birnin Abuja.

Sanarwar da jami’in hulda da jama’a na hukumar ‘yan sandan jihar Zamfara, DSP Muhammad Shehu, ya bayar a ranar Juma’a, 24 ga watan Nuwamba, ta nuna cewa sabon kwamishinan ‘yan sandan ya ziyarci wuraren da ake rikici nan da nan don tsara yadda za a magance matsalolin yankin.

Hukumar ‘yan sanda
Ya ce, “Mun ziyarci yankin karamar hukumar Shinkafi daya daga cikin kananan hukumomin da ‘yan bindigar da ba a sani ba, suka kai hari a makon jiya”.

Ya ce sabon kwamishinan ya yi ziyarar ta’aziyya zuwa ga sarkin Shinkafi, Alhaji Muhammad-Makwashe Isah, game da hare-haren kwanan nan da kuma rasa rayuka, ya kuma kira ga goyon baya da hadin kai daga masarautar.

Kwamishinan, wanda ya sadu da shugabanni al’ummar yankin, ya yi alwashin gano da kuma hukunta wadanda suka aikata laifuffukan, ya kuma yi alkawarin karfafa harakar tsaro a jihar.

Idan dai baku manta ba a makon da ta gabat Labaran Duniya.Com ta ruwaito cewa ‘yan bindigar da ba a san su ba sun kai hari kan wasu garuruwa da ke yankin kananan hukumomin Shinkafi da Maradun a ranar Juma’a da Asabar da ta gabata, inda suka kashe mutane da dama.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...