Skip to main content

‘An Mayar Da Mu Saniyar Ware’ — Niger Delta







Wasu Shugabannin a yankin Neja Delta na ci gaba da tofa albarkacin bakin su dangane da barazanar da wasu masu tada kayar baya a yankin suka yi cewa zasu koma farfasa bututan mai a yankin.

Farfesa Akasoba Zainab Duke-Abiola, matar wani basarake ce a yankin, kuma shugabar wata kungiyar wanzar da zaman lafiya a Najeriya, ta shaida wa BBC cewa, duk da kundin tsarin mulkin kasa ya basu damar su yi bore, ai bai ba su damar su tayar da hankalin jama’a ba.

Ta ce abin da ta ke gani ya harzuka masu tayar da bayan har suka yi wannan barazana shi ne, saboda ba a kula da su, an mayar da su saniyar ware tamkar baki a cikin kasarsu.

Farfesar ta ce, duk wani tago mashi da ‘yan Najeriya ke samu, ba bu ‘yan yankin Neja Delta a ciki,don haka me ake so suyi? gwamnati ce yakamata ta dubi lamarinsu.

Shugabar kungiyar ta ce, ba bu wani kwakkwaran shugabanci a yankin Neja Delta, shi ya sa ganin shugaban kasa ma su kai kokensu ke musu matukar wuya.

Farfesa Akasoba, ta ce yakamata a hadu da ainihin shugabannin da suka fito daga yankin don a lalubo bakin zaren matsalolin da yankin na Neja Delta ke fama da su, saboda gaskiya tura na kai wa bango.

Ta ce mutanen yankin ba su da isasshen abinci, don hatta masara idan aka dafa ba a cinta cikin dadi saboda fetur din da ake haka a yankin na su na bata musu abinci.

Shugabar kungiyar ta ce, baya ga rashin abinci, hatta ruwan sha mai tsafta ba su dashi a yankin, saboda hakar mai.

Farfesa Zainab ta ce, duk da wadannan matsaloli da yankin na su ke fuskanta, tana mai bawa masu fasa bututan mai shawara a kan su daina fasawa su kuma daina abinda suke yi saboda yin hakan ba a dauko hanyar zaman lafiya ba.

A bangaren gwamnatin kuma farfesar ta ce, yakamata gwamnati ta tattauna da mutanen da ya kamata, sannan ayi kokarin karbe sauran makaman da ke hannun masu tayar da kayar baya.

A kwanakin baya ne dai gwamnatin Najeriya ta ce a shirye take ta zauna da masu tayar da kayar bayan don jin korafin su game da matsalolin da suka addabi yankin.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...