Skip to main content

‘An Mayar Da Mu Saniyar Ware’ — Niger Delta







Wasu Shugabannin a yankin Neja Delta na ci gaba da tofa albarkacin bakin su dangane da barazanar da wasu masu tada kayar baya a yankin suka yi cewa zasu koma farfasa bututan mai a yankin.

Farfesa Akasoba Zainab Duke-Abiola, matar wani basarake ce a yankin, kuma shugabar wata kungiyar wanzar da zaman lafiya a Najeriya, ta shaida wa BBC cewa, duk da kundin tsarin mulkin kasa ya basu damar su yi bore, ai bai ba su damar su tayar da hankalin jama’a ba.

Ta ce abin da ta ke gani ya harzuka masu tayar da bayan har suka yi wannan barazana shi ne, saboda ba a kula da su, an mayar da su saniyar ware tamkar baki a cikin kasarsu.

Farfesar ta ce, duk wani tago mashi da ‘yan Najeriya ke samu, ba bu ‘yan yankin Neja Delta a ciki,don haka me ake so suyi? gwamnati ce yakamata ta dubi lamarinsu.

Shugabar kungiyar ta ce, ba bu wani kwakkwaran shugabanci a yankin Neja Delta, shi ya sa ganin shugaban kasa ma su kai kokensu ke musu matukar wuya.

Farfesa Akasoba, ta ce yakamata a hadu da ainihin shugabannin da suka fito daga yankin don a lalubo bakin zaren matsalolin da yankin na Neja Delta ke fama da su, saboda gaskiya tura na kai wa bango.

Ta ce mutanen yankin ba su da isasshen abinci, don hatta masara idan aka dafa ba a cinta cikin dadi saboda fetur din da ake haka a yankin na su na bata musu abinci.

Shugabar kungiyar ta ce, baya ga rashin abinci, hatta ruwan sha mai tsafta ba su dashi a yankin, saboda hakar mai.

Farfesa Zainab ta ce, duk da wadannan matsaloli da yankin na su ke fuskanta, tana mai bawa masu fasa bututan mai shawara a kan su daina fasawa su kuma daina abinda suke yi saboda yin hakan ba a dauko hanyar zaman lafiya ba.

A bangaren gwamnatin kuma farfesar ta ce, yakamata gwamnati ta tattauna da mutanen da ya kamata, sannan ayi kokarin karbe sauran makaman da ke hannun masu tayar da kayar baya.

A kwanakin baya ne dai gwamnatin Najeriya ta ce a shirye take ta zauna da masu tayar da kayar bayan don jin korafin su game da matsalolin da suka addabi yankin.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.