Skip to main content

Nijeriya Za Ta Iya Amfana Da Tsarin Shugabancin Ƙasar Mexico —Ikweremadu


Nijeriya Za Ta Iya Amfana Da Tsarin Shugabancin Ƙasar Mexico —Ikweremadu

Daga Bello Hamza

Mataimakin shugaban Majalisar dattawa ta ƙasa, Ike Ekweremadu, ya bayyana cewa, Nijeriya za ta yi natsarin tsarin mulkin ƙasar Mexico na yin shugabanci sau ɗaya ga shugaban ƙasa da gwamnoni, domin fahimtar ko akwai wata moriyar da za ta ci daga irin wannan tsari.

Ekweremadu, ya bayyana hakan ne lokacin da Ambasadan Mexico a Nijeriya, Garcia Moreno Elizondo, ya kawo masa ziyara a Abuja, don taya shi murnar cika shekara 57 da samun mulkin kai a Nijeriya.

Ya ce, Nijeriya da Meɗico na da abubuwa da yawa da za su amfani junanasu da su, musamman ta fuskar arziƙin wadataccen da kuma tsarin gwamnatin tarayya.

A cikin jawabin wanda mai bai wa mataimakin shugaban Majalisar  shawara na musamman  a kan harkokin yaɗa labarai, Uche Anichukwu, Special, ya bayyana cewa, mataimakin shugaban Majalisar ya ce, “Na daɗe da sanin cewa, ƙasar Mexico na da tsarin yin shugaban ƙasa na shekara shida sau ɗaya tak, wanda suke kiransa “seɗino”. Wannan tsari da Nijeriya za ta yi nazari a kansa, saboda akwai matsaloli tattare da tsarin da muke bi a halin yanzu.

“Saboda haka muna duba yiwuwar gyara tsarin mulkinmu wanda zai tabbatar da yin shugaban ƙasa sau ɗaya, don mu rage yawan kashe kuɗin da ake yi wajen gudanar da zaɓuɓɓuka, da gogoriyon neman dawo wa, don a rage almubazzaranci da dukiyar gwamnati”.

“Za mu so mu ji ƙarin haske a gurinka dangane da yadda kuke amfana da tsarin shugabancin ƙasa sau ɗaya, don mu haɗa kai mu ga yadda za mu amfana da irin wannan tsarin”.

Ekweremadu, ya ci gaba da cewa, ya lura jihohi a Mexico na cin gashin kansu  wanda tsarin mulkin ƙasar ya tada musu, saboda haka ƙasar za ta zama mudubi a wajenmu domin amfana da hikimarsu ta gudanar da mulki.

“Saboda haka yanzu za mu ga abin da za mu na ƙarfafa wa jihohi, har ma da ƙananan hukumomi, domin mu rage wa gwamnatin tarayya nauyin da ke kanta. Daga cikin abin da za mu yi na bai wa ƙananan hukumomi cin gashin kansu shi ne, su dinga samun kuɗinsu kaitsaye daga gwamnatin tarayya”.

“Nakan samu kuɗin ƙaramar hukuma ta kaitsaye daga gwamnatin tarayya a matsayina na shugaban ƙaramar hukuma kafin shekara ta 1999. Amma a shekara ta 1999 sai abu ya canza, lokacin da aka kawo wani tsari na asusun haɗaka tsakanin jihohi da ƙananan hukumomi”.

“Sai dai ko a wancan lokacin wasu jihohin sun fake da yin wasu ayyukan da ƙananan hukumomin ke buƙata maimakon su ba su kuɗinsu su yi ayyukansu da kansu. Saboda haka, yanzu za mu yi ƙoƙarin farfafɗo da wancan tsari yadda ƙananan hukumomi za su samu damar tsayawa da ƙafafunsu”

Ekweremadu  ya ci gaba da cewa, Majalisar tarayya za ta ci gaba da ƙoƙarin da take na ganin an samu cin ribar dimokaraɗiyya yadda kowane ɓangare zai samu ‘yancin kansa.

A ƙarshe ambasadan na ƙasar Mexico Elizondo, ya ce, Nijeryia da Mexico na fuskantar ƙalubale iri ɗaya, na ƙoƙarin bunƙasa rayuwar ‘yan ƙasa, saboda haka, in aka zauna aka tattauna za a amfana da juna kamar yadda ya ce.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.