Skip to main content

Kasar Masar Ta Ba Wa Kanawa Kyautar Gurbin Karatu

Kasar Masar Ta Ba Wa Kanawa Kyautar Gurbin Karatu

Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranci mika takardun tallafin karatu ga yan asalin jihar Kano guda takwas 8 a jami'ar Al-Azhar dake garin Alkahira, wanda gwamnatin Masar ta bayar.

Gwamna Ganduje ya yabawa gwamnatin Masar bisa wannan tallafi na karatu da ta bayar, wanda shine karo na biyu da suka bayar, domin taimakawa ma su karamin karfi, don su karo ilimi. Hakazalika Gwamna Ganduje ya ce bai yi mamaki ba, ganin irin dumbin tarihin da ke tsakanin Kano da kasar Masar, shekaru da dama.

Gwamnan ya ci gaba da cewa yanayin tatabarbarewar tattalin arziki ya sa jihar Kano ta dakatar da tura dalibai karatu kasar waje, inda a har yanzu gwamnati na kokarin sauke nauyin da ta gada ne na daliban da aka tura kasashen waje a gwamnatin baya, saboda haka irin wannan tallafi zai taimaka kwarai wajen ganin an taimakawa masu karamin karfi domin karo ilimi a waje. Daga bisani Gwamnan yayi kira ga daliban da su maida hankali wajen karatun su, kuma Ya baiyana cewa gwamnatin sa zata bawa kowanne dalibi dala dubu daya guzuri.

A nasa jawabin, wakilin kasar Masar kuma shugaban hukumar raya al'adu na kasar masar reshin jihar Kano Dr Ibrahim Ibrahim ya ce wannan tallafi da suka bawa wadannan dalibai su 8, tafi da gidan ka ne hade da kudin makaranta, kudin masauki, kudin abinci, inshora ta lafiya, tikiti na zuwa da komowa, harda kudin kashewa duk wata.

Dr Ibrabim ya kara da cewa, hudu daga cikin daliban zasu shiga makarantar gaba da firamare ne har zuwa jami'a, sannan hudu kuma daga jami'a za su fara. Ya kara da cewa gwamnatin su a shirye suke domin samar wa da wadannan dalibai yanayi mai inganci don ganin sun kammala karatun su cikin nutsuwa.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...