Skip to main content

Kasar Masar Ta Ba Wa Kanawa Kyautar Gurbin Karatu

Kasar Masar Ta Ba Wa Kanawa Kyautar Gurbin Karatu

Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranci mika takardun tallafin karatu ga yan asalin jihar Kano guda takwas 8 a jami'ar Al-Azhar dake garin Alkahira, wanda gwamnatin Masar ta bayar.

Gwamna Ganduje ya yabawa gwamnatin Masar bisa wannan tallafi na karatu da ta bayar, wanda shine karo na biyu da suka bayar, domin taimakawa ma su karamin karfi, don su karo ilimi. Hakazalika Gwamna Ganduje ya ce bai yi mamaki ba, ganin irin dumbin tarihin da ke tsakanin Kano da kasar Masar, shekaru da dama.

Gwamnan ya ci gaba da cewa yanayin tatabarbarewar tattalin arziki ya sa jihar Kano ta dakatar da tura dalibai karatu kasar waje, inda a har yanzu gwamnati na kokarin sauke nauyin da ta gada ne na daliban da aka tura kasashen waje a gwamnatin baya, saboda haka irin wannan tallafi zai taimaka kwarai wajen ganin an taimakawa masu karamin karfi domin karo ilimi a waje. Daga bisani Gwamnan yayi kira ga daliban da su maida hankali wajen karatun su, kuma Ya baiyana cewa gwamnatin sa zata bawa kowanne dalibi dala dubu daya guzuri.

A nasa jawabin, wakilin kasar Masar kuma shugaban hukumar raya al'adu na kasar masar reshin jihar Kano Dr Ibrahim Ibrahim ya ce wannan tallafi da suka bawa wadannan dalibai su 8, tafi da gidan ka ne hade da kudin makaranta, kudin masauki, kudin abinci, inshora ta lafiya, tikiti na zuwa da komowa, harda kudin kashewa duk wata.

Dr Ibrabim ya kara da cewa, hudu daga cikin daliban zasu shiga makarantar gaba da firamare ne har zuwa jami'a, sannan hudu kuma daga jami'a za su fara. Ya kara da cewa gwamnatin su a shirye suke domin samar wa da wadannan dalibai yanayi mai inganci don ganin sun kammala karatun su cikin nutsuwa.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.