Skip to main content

An Kashe Sojojin Amurka A Nijar

An Kashe Sojojin Amurka A Nijar

Wasu mahara daga kasar Mali sun yi wa dakarun Nijar da na Amurka kwanton-bauna a garin Tongo Tongo da ke arewacin jahar Tillabery, inda suka kashe sojin Amurka uku da na Nijar biyar, wasu kuma ba a gansu ba a harin da aka kai ranar Laraba.

Rahotanni sun ce 'yan bindigar daga Mali sun kai farmaki ne garin da ke kan iyakar Nijar da Mali a ranar Laraba da yamma, amma dakarun Nijar da na Amurka da ke yankin suka koro su.
A yayin wannan raraka ne da dakarun na Nijar da Amurkar suka yi musu ne sai 'yan tawayen suka yi musu kwanton-bauna, suka halaka wasu, sannan kuma ba a ga wasunsu ba.

Ya zuwa yanzu dai babu wani cikakken bayani game da lamarin da hukumomin Nijar suka fitar.
Sojojin Amurka suna bayar da horo da sauran taimako ga takwarorinsu na Nijar domin taimaka musu a yaki da mayaka masu ikirarin jihadi, wadanda suka hada da reshen kungiyar Al Qaeda na Arewacin Afirka.

A wani rahoto da Majalisar dinkin duniya ta fitar a baya bayan nan ta ce hare-haren da masu kaifin kishin Islama ke kai wa dakarun gwamnatin Mali da dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya da ma dakarun Faransa na kara karuwa matuka gaya.
An kai irin wadannan hare-hare guda 75 a tsakanin watan Yuni zuwa Satumbar da ya gabata, lamarin da ya rubanya na watanni hudu kafin watan Yunin.

An bayyana shirin wanzar da zaman lafiya na majalisar dinkin duniya a Mali da cewa shi ne mafi muni a duniya.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

A SAMARWA DA 'YAN GUDUN HIJIRA DA MASAUKAI!

A bisa ma'aunin Ilimi da hangen nesa, duk wanda ya baro garinsu, inda komai nasa a ce yake, kamar 'yan Uwansa da abokansa, mahaifansa, wadanda suke a raye da kuma wadanda Allah yayi rasuwa, kuma ya baro abincinsa wanda zaici, ya baro dabbobinsa wadanda ya dogara da su, Kacokan! ya fantsama yayi kaura zuwa wani waje, inda shima kansa bai san inda ya maida gaba ba, ina ganin wannan shine mafi munin tashin hankali da firgici da ɗimauta. A kullum a duk inda ka duba zakaga 'yan gudun Hijira ne birgik a saman tituna suna yawon barace-barace cikin kaskance da takaici, musamman yara 'yan Dagwai-dagwai wasunsu ma basu dade da fara iya tafiya ba, suna neman a taimake su, da abinda zasu ci, wasu daga cikinsu ko takalmin sakawa basu da haka nan suke yawo a Kasa cikin tagaiyara da nadama. Haka idon mukayi la'akari da yadda idon mutun ya saba da wajen zamansa akace ya tashi yabar wurin ba tare da kintsawa ba, yaya yake ji a cikin ransa? A 'yan baya-bayan nan shekaru biy...

ZAMU FADADA SHIRINMU NA YAZEED TRUST FUND MATERNITY CARE.......

Garkuwan matasan Gusau,Lamidon Tsafe wato Yazeed shehu Danfulani Mai Doya Gusau,ya jaddadar da ya zabi yaci gaba da zama hadimin al'umma arayuwarsa tare da bayyanar da kudurinsa akan baiwa lafiya fifiko musamman awannan lokaci da rayuwa ta soma tsada ga rayuwar bayin Allah sanadiyar cutar COVID-19. Lamidon Tsafe Yazeed Shehu Danfulani ya nuna tausayinsa ga yanda al'umma ke samun karancin shigar riba musamman Masu kananan sana'oin hannu,tare da tsaiko akan dakatuwar kasuwancinsu a wajen jahar zamfara(Yan fatauci). Hakan yasa Yazeed Danfulani yabada Umurnin fadada shirinsa na TAIMAKAWA MATA MASU DAUKE DA JUNA BIYU tare da fadakarwa akan hanyoyin kiyaye Lafiyar juna biyu da matakan dauka ayayin renon juna biyu,tare da bada Magunna Fisabilillah da fatar Allah saukar lafiya. Allah karfafa yasakama Yazeed da mafificin alhairi. YAZEED TRUST FUND. Rufai UB Gusau. 08106580400.