Skip to main content

An Kashe Sojojin Amurka A Nijar

An Kashe Sojojin Amurka A Nijar

Wasu mahara daga kasar Mali sun yi wa dakarun Nijar da na Amurka kwanton-bauna a garin Tongo Tongo da ke arewacin jahar Tillabery, inda suka kashe sojin Amurka uku da na Nijar biyar, wasu kuma ba a gansu ba a harin da aka kai ranar Laraba.

Rahotanni sun ce 'yan bindigar daga Mali sun kai farmaki ne garin da ke kan iyakar Nijar da Mali a ranar Laraba da yamma, amma dakarun Nijar da na Amurka da ke yankin suka koro su.
A yayin wannan raraka ne da dakarun na Nijar da Amurkar suka yi musu ne sai 'yan tawayen suka yi musu kwanton-bauna, suka halaka wasu, sannan kuma ba a ga wasunsu ba.

Ya zuwa yanzu dai babu wani cikakken bayani game da lamarin da hukumomin Nijar suka fitar.
Sojojin Amurka suna bayar da horo da sauran taimako ga takwarorinsu na Nijar domin taimaka musu a yaki da mayaka masu ikirarin jihadi, wadanda suka hada da reshen kungiyar Al Qaeda na Arewacin Afirka.

A wani rahoto da Majalisar dinkin duniya ta fitar a baya bayan nan ta ce hare-haren da masu kaifin kishin Islama ke kai wa dakarun gwamnatin Mali da dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya da ma dakarun Faransa na kara karuwa matuka gaya.
An kai irin wadannan hare-hare guda 75 a tsakanin watan Yuni zuwa Satumbar da ya gabata, lamarin da ya rubanya na watanni hudu kafin watan Yunin.

An bayyana shirin wanzar da zaman lafiya na majalisar dinkin duniya a Mali da cewa shi ne mafi muni a duniya.

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM GLOBAL INITIATIVES .... PRESS RELEASE ...

Good day Ladies and Gentlemen of the media.                       In the past few days, we were surprised to learn that few among our Foundation members posted online their official statement of resignation from Labour room cabinet. Despite mixed feelings, Let us start by stating the following: 1. We hereby acknowledge your  contributions to the dynamics of the Labour room. Though, letters were served to each and every appointment/portfolio. Its expected that you write to Labour room Leadership about your intentions rather than addressing it to the general public, but nonetheless, its all for good. 2. The leadership of the labour room global initiatives remain focused, as all those that resigned constitute less than 3% of the entire cabinet. 3. We remain committed to d service to humanity 4. Those outsiders that are not acquainted with the processes of the labour room and genesis of the matter should always endeav...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...