Skip to main content

Gwamnan Zamfara Yari Ya Tsayar Da Tawagarsa Don Tallafawa Wadanda Hatsarin Mota Ya Rutsa Da Su A Hanya

Gwamnan Zamfara Yari Ya Tsayar Da Tawagarsa Don Tallafawa Wadanda Hatsarin Mota Ya Rutsa Da Su A Hanya

Daga Yusuf Abubakar, Sokoto

Gwamnan jahar Zamfara, Alhaji Abdulazeez Yari Abubakar wanda ke akan hanya daga Talata Mafara zuwa Sokoto ya tsayar da tawagar ayarinsa don bayar da taimakon gaggawa ga wasu mutane da hatsarin mota ya rutsa dasu akan hanya kusa da 'Dogon Awo' na hanyar Talata Mafara zuwa Sokoto da safiyar yau Talata.

Gwamna Yari wanda ya fito a cikin ruwan sama har ya jike sharkaf yayin da yake bayar da umurnin kwashe wadanda suka ji raunuka, mussaman wani dan karamin yaro dan shekaru 8 a duniya.

Gwamna Yari ya bayar da gudumuwa naira dubu dari biyar anan take tare da umurnin motar daukar marasa lafiya ta gidan gwamnati jahar Zamfara dake tare da ayarinsa da ta kwashe wadanda suka yi raunuka zuwa Babban Asibitin garin Talata Mafara.

Masu bayar da agaji (wanda ya kunshi mai rubutun) sun shafe mintuna fiye da talatin  suna jiran zuwan taimakon jami'an hukumar kiyaye haddura ta kasa FRSC, amma babu kamin isowar ayarin na gwamna Abdul-Azeez Yari wanda suka taimaka.

Babu wani jami'a ko daya da yazo duk da wayar da aka buga a ofishin FRSC dake Mafara abin da bai fi kilomita 20 da inda akayi hatsarin ba.

A karshe babu wani taimako sai da Allah Ya kawo gwamnan jahar Zamfara, Abdul'azeez Yari wanda ya tsaya da kansa tare da jami'ansa suka taimaka da motar daukar maras lafiya.

Haka ma ya bayar da gudumuwa na naira dubu dari biyar garesu don taimaka masu sayen magani.

Abin takaici har gwamna da sauran jama'a suka bar wurin da akayi hatsarin babu jami'in hukumar FRSC ko daya wanda yazo duk da yake suna da motar bas da aka tanada don daukar wadanda suka yi hatsari akan wannan hanyar.

Mafi rinjaye jama'a a wurin sun jijjinawa gwamna Yari dangane da kwashe mintuna har fiye da arba'in a cikin ruwan sama yana aikin ceto ga wadanda suka yi hatsari.

Haka ma ya dace jami'an hukumar FRSC na garin Mafara dasu gyara lamarin aikinsu da bayar da agajin gaggawa lokacin da ake bukatarsa don ceto rayuka.

Babu wanda ya rasu a lokacin hatsarin, amma kusan dukkan wadanda ke cikin motar da tayi hatsari sun ki mummunan rauni ga jikinsu.

Yusuf Abubakar
Dan jarida ne

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

Coronavirus; Me kuke so ku sani kan matakan kariya daga cutar Covid19

Wadan ne abubuwa ne kuke so ku sani, sannan wadanne matakan kariya kuke so ku sani kan wannan cuta  Ya  gwamnatin Najeriya ta hana mutane baki shiga da fita a kasar nan sannan gwamnati ta fara gudanar da bincike domin gano ko akwai mutanen da suka kamu da cutar a dalilin yin mu’amula da dan kasar Italy a jihohin Legas da Ondo. Daga nan hukumar hana yaduwar cututtuka ta yi kira ga mutane da su kiyaye hanyoyin samun kariya daga kamuwa da cutar da hukumar ta bada. HANYOYIN SAMUN KARIYA DAGA CUTAR: 1. Yawaita wanke hannu da ruwa da sabullu ko kuma da man tsaftace hannu ‘Hand Sanitizer’ idan babu ruwa. 2. A rika tsaftace muhalli. 3. Idan za a yi tari ko kuma atishawa a yi amfani da tsumma domin kare baki da hanci. 4. A guji yawan kusantan mai fama da mura ko kuma alamomin cutar. 5. Wurarren aiki su tabbatar sun ajiye ruwa da sabullu domin ma’aikata su rika wannke hannu ko kuma a ajiye man tsaftace hannu. 6. A guji shan magani ba tare da izinin likita ba. ...

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province

Pakistani Campaigner for the ‘Disappeared’ Himself Goes Missing Four Activists Feared Forcibly Disappeared in Sindh Province Saroop Ijaz It was only last month when Punhal Sario marched from the Pakistani cities of Hyderabad to Karachi to demand the return of fellow activists who had gone “missing,” a Pakistani euphemism for those forcibly disappeared by the state authorities. Now, Sario himself is feared missing . Witnesses say that Sario, a 58-year-old human rights activist and head of the Voice for Missing Persons of Sindh, was abducted from Hyderabad by security forces on August 3. Four days later, men in plainclothes accompanied by police officials abducted three other people – Partab Shivani, a teacher and activist; Naseer Kumbhar, a writer; and Mohammad Umer, a political party worker – from the Tharparkar district of Sindh province. Pakistani authorities deny any involvement, but have produced no information on the men’s whereabouts. In a further show of intimidation of cri...