Skip to main content

Gwamnan Zamfara Yari Ya Tsayar Da Tawagarsa Don Tallafawa Wadanda Hatsarin Mota Ya Rutsa Da Su A Hanya

Gwamnan Zamfara Yari Ya Tsayar Da Tawagarsa Don Tallafawa Wadanda Hatsarin Mota Ya Rutsa Da Su A Hanya

Daga Yusuf Abubakar, Sokoto

Gwamnan jahar Zamfara, Alhaji Abdulazeez Yari Abubakar wanda ke akan hanya daga Talata Mafara zuwa Sokoto ya tsayar da tawagar ayarinsa don bayar da taimakon gaggawa ga wasu mutane da hatsarin mota ya rutsa dasu akan hanya kusa da 'Dogon Awo' na hanyar Talata Mafara zuwa Sokoto da safiyar yau Talata.

Gwamna Yari wanda ya fito a cikin ruwan sama har ya jike sharkaf yayin da yake bayar da umurnin kwashe wadanda suka ji raunuka, mussaman wani dan karamin yaro dan shekaru 8 a duniya.

Gwamna Yari ya bayar da gudumuwa naira dubu dari biyar anan take tare da umurnin motar daukar marasa lafiya ta gidan gwamnati jahar Zamfara dake tare da ayarinsa da ta kwashe wadanda suka yi raunuka zuwa Babban Asibitin garin Talata Mafara.

Masu bayar da agaji (wanda ya kunshi mai rubutun) sun shafe mintuna fiye da talatin  suna jiran zuwan taimakon jami'an hukumar kiyaye haddura ta kasa FRSC, amma babu kamin isowar ayarin na gwamna Abdul-Azeez Yari wanda suka taimaka.

Babu wani jami'a ko daya da yazo duk da wayar da aka buga a ofishin FRSC dake Mafara abin da bai fi kilomita 20 da inda akayi hatsarin ba.

A karshe babu wani taimako sai da Allah Ya kawo gwamnan jahar Zamfara, Abdul'azeez Yari wanda ya tsaya da kansa tare da jami'ansa suka taimaka da motar daukar maras lafiya.

Haka ma ya bayar da gudumuwa na naira dubu dari biyar garesu don taimaka masu sayen magani.

Abin takaici har gwamna da sauran jama'a suka bar wurin da akayi hatsarin babu jami'in hukumar FRSC ko daya wanda yazo duk da yake suna da motar bas da aka tanada don daukar wadanda suka yi hatsari akan wannan hanyar.

Mafi rinjaye jama'a a wurin sun jijjinawa gwamna Yari dangane da kwashe mintuna har fiye da arba'in a cikin ruwan sama yana aikin ceto ga wadanda suka yi hatsari.

Haka ma ya dace jami'an hukumar FRSC na garin Mafara dasu gyara lamarin aikinsu da bayar da agajin gaggawa lokacin da ake bukatarsa don ceto rayuka.

Babu wanda ya rasu a lokacin hatsarin, amma kusan dukkan wadanda ke cikin motar da tayi hatsari sun ki mummunan rauni ga jikinsu.

Yusuf Abubakar
Dan jarida ne

Comments

Popular posts from this blog

Babban burinmu a wannan shekara ta 2020

Masana sun ce daga cikin abubuwan da suka sa dan Adam yin galaba a kan sauran halittu shi ne yadda yake iya hada kai. Don mutum shi kadai ba zai iya gwada karfi da zaki ko giwa ba. Amma idan ya hada karfi da sauran ‘yan uwansa babu kalubalen da ba za su iya tinkara ba. Hadin kai kuma ba ya tabbata sai da yarda, kuma yarda sai da mu’amala. Masu hikimar magana sun ce, Allah Ya halicce mu da kunne biyu, ido biyu amma sai ya yi mu da baki daya domin mu kalla, mu kuma saurara fiye da yadda muke magana.  Amma sai ya kasance cewa mun fi son yin magana fiye da saurare. Sau da yawa idan muna tattaunawa da wadansu ba ma mayar da hankali kan abin da ake fadi. Kawai jira muke mutum ya kai aya - idan ba mu katse shi ba kenan, domin mu fadi namu ra’ayin. Ga shi kuma ba mu son jin ra’ayoyin da suka sha bamban da namu. To ina za a samu fahimtar juna har a yi aiki tare?  Babu wanda rayuwarsa iri ɗaya da ta wani, kowa da irin  jarabawar shi,  kowa kuma da irin ta shi f...

LABOUR ROOM BLOBAL INITIATIVE KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MATASA DA 'YAN SIYASA

Duk tarin dukiyarka, ko girman mulkinka ko zamanka basarake, ba zaka taɓa jin daɗin abinda kake taƙama da shi ba, matuƙar al`ummar da kake rayuwa a cikinta ba su zaune lafiya ko da kai ka tsira, kuwa. Shi dama talaka juji ne, duk wani tarin dattin tashin hankali, akansa yake ƙarewa. Da shi ake amfani wajen tashe-tashen hankula, shi ke kisa kuma shi ake kashewa kuma duk masifar da kan biyo baya a kansa ne take sauka. In ko haka ne, haƙiƙa da sake! kenan kowa na matuƙar kaunar zaman lafiya a cikin al'umma, domin sai da zaman lafiya ɗin ne, kowa zai iya morewa, har ya iya rayuwarsa ba tare da shiga tasko ba. A kan haka ne! Ƙungiyar Labour Room Global Initiative haɗin gwiwa da Ƙungiyoyin Jihar Zamfara ke amfani da wannan damar wajan kira ga dukkanin 'yan Siyasa, da ayi siyasa ba tare da gaba ba. Domin in dai har za'a iya zubar da jini a kashe rai a zaɓen fitar da gwani kurrum na jam'iyya ɗaya, to ina ga zaɓen gama-gari da ke tafe? Don haka muna amfani da wannan ...

MUNA JIMAMIN RASHIN 'YAR ADU'A

hakika tarihi ba zai taba mantawa da tsohon shugaban Kasar Najeriya ba, margayi Alh Umar Musa 'yar Adu'a, kasancewarsa duk da baiyi wani dadewa ba a kan karagar jagorancin kasar nan, amma Najeriya ta shedi gwagwarmayarsa, ta fannoni da dama. Idan muka yi la'akari da yadda ya zage damtse wajan fafutikar ganin Najeriya ta zauna lafiya, musamman rikice-rikicen 'yan tawayen Niger-Delta da sauransu. Idan muka dubi fannin samar da ilimi wanda a nan sashen yayi rawar gani, haka a fannin kiyon lafiya da cigaban rayuwa. Lokacin Alh Umar Musa 'yar'adua yana shugaban kasa talakawa da dama sun dara, kasancewar yayi yunkurin ganin kasar nan ta samu cigaba ta kowane fanni. Muna fatan Allah yaji kanshi ya masa rahama ya sanya aljanna ta kasance makoma a gareshi. Najeriya tayi babban rashi. Daga Nura Muhammad Mai Apple Gusau 08133376020